Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 23 ga watan Yuli, 2026.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammad

  1. Mun kai sabbin hare-hare kan sansanonin Amurka a Kuwait - Sojin Iran

    Sashen yaɗa labarai na rundunar juyin juya hali ta Iran ya ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana cewa ƙasar ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan sansanonin sojin Amurka uku a ƙasar Kuwait.

    Bayanin ya ce sansanonin su ne: Sansanin sojin Ali al-Salem da kuma na Arifjan, wadanda aka yi amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai musu hari a yau.

    Sai kuma sansanin Doha, wanda ya ƙunshi rumbun ajiye makamai da kayan aiki na sojojin Amurka.

  2. An kwashe dare na 12 ana musayar wuta tsakanin Iran da Amurka

    Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare a kan Iran na dare na 12 a jere. Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa an ji ƙarar fashewa a kusa da birnin Bushehr.

    Iran ma ta ci gaba da mayar da martani, inda ƙasar Kuwait ta ce garkuwarta ta sararin samaniya ta yi nasarar kakkaɓe wasu jirage marasa matuƙa da ta bayyana a matsayin na abokan gaba.

    Dakarun juyin-juya-hali na Iran sun yi ikirarin cewa wani jirgin dakon ɗanyen mai ya kama da wuta a wani yanki da aka dasa nakiyoyi a kusa da mashigar Hormuz, yayin da wasu jiragen dakon mai biyu suka juya baya.

    Jami’an tsaron Iran sun sake jaddada cewa ba za a bari wani jirgin dakon mai ya ratsa Mashigar ba, ba tare da haɗin kai ko amincewar Iran ba.

  3. Ƙungiyar Houthi mai goyon bayan Iran ta fara kai wa jiragen ruwa hari

    Ƙungiyar Houthi da ke Yemen, wadda Iran ke mara wa baya, ta ce ta kai hari kan jiragen ruwa na dakon mai na Saudiyya guda biyu a tekun Maliya.

    Dama akwai rahotanni da ke cewa wasu jiragen ruwa na dakon mai na sauya hanya, bayan da mayaƙan Houthi suka gargaɗi jiragen ruwa da su kauce wa tashoshin ruwa na Saudiyya.

    Kamfanin dillancin labarai na hukumar Saudiyya ya tabbatar da cewa harin da aka kai ya samu ɗaya daga cikin jiragen, mai suna Encelia, har gobara ta tashi a cikinsa.

    Saudiyya ta bayyana harin a matsayin saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.

    A halin yanzu, akwai ƙarin fargaba cewa matakin da mayakan Houthin ke ɗauka na hana zirga-zirgar jiragen ruwa zai iya haddasa tashin gwauron zabi a farashin man fetur a duniya.

  4. Barka da warhaka!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye a wannan rana ta Alhamis - Tabawa ranar samu- inda muke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya shiga zaurenmu na BBC Hausa WhatsApp domin samun labarai da ɗumi-ɗuminsu kuma ku yi shiyarin.

    Haka nan za ku iya tofa albarkacin bakinku a shafukanmu na facebook, instagram, X da kuma YouTube.