Waɗanda suka kamu da cutar Ebola a DR Congo sun haura 1700 tare da kashe aƙalla mutum 600

Asalin hoton, Amensisa Ifa / BBC
Yawan mutanen da suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ya karu zuwa dubu daya da dari bakwai da hamsin da tara.
Ya zuwa yanzu, mutum 600 ne suka mutu sakamakon barkewar cutar ta yanzu.
Haka kuma an tabbatar da samun mutum biyu da suka kamu da cutar a wani lardi, lamarin da ke nuna cewa cutar na ci gaba da bazuwa lardin Tshopo da ke yammacin kasar.
A baya dai cutar ta fi kamari a yankin arewa maso gabashin ƙasar.















