Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 14/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 14/07/2026

Taƙaitattu

  • Dangote ya fara sayar da man fetur da dala
  • An ji ƙarar manyan abubuwan fashewa a Iran
  • Sojojin Jordan sun ce sun kakkaɓo makaman Iran
  • Ƙasashen Gulf za su fara biyan kuɗin tsaron da muke ba su - Trump
  • Iran ta ce ta kai hare-haren kan manyan jiragen dakon mai a mashigar Hormuz
Skip Bidiyo and continue reading
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Ƙungiyoyin kare muhalli na son Dangote ya dakatar da shirin gina matatar mai a Kenya

    Dangote

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar kare muhalli ta Greenpeace Africa ta buƙaci attajirin Afirka, Aliko Dangote, ya dakatar da shirin gina wata babbar matatar man fetur a yankin gabar tekun Kenya, inda ta ce aikin na iya haifar da mummunar illa ga muhalli.

    A farkon watan nan ne aka tabbatar da cewa za a gina matatar, wadda ake sa ran za ta tace ganga 700,000 na ɗanyen mai a kullum, a tashar jiragen ruwa ta Lamu da ke Kenya, bayan watanni ana ta hasashen ko a Tanzania ne za a gina ta.

    "Aikin na barazana ga ɗaya daga cikin muhallin gabar teku mafi muni a Gabashin Afirka, kuma hakan zai jefa yanayin Kenya zuwa mafi muni," in ji mai fafutukar yaƙi da harkokin mai da iskar gas ta Greenpeace Africa, Sherelee Odayar.

    Ƙungiyar ta ce matatar da ake sa ran za a ɗauki kusan watanni 30 ana gina ta za ta iya haifar da lalacewar muhalli, gurɓacewar tekuna, kwararar mai da kuma gurbatar iska.

    Greenpeace Africa ta buƙaci a dakatar da aikin mai darajar dala biliyan 17, har sai an gudanar da cikakken bincike kan tasirin da zai iya yi ga muhalli da al'umma.

    "Bai kamata a amince da fara aikin ba sai bayan an kammala cikakken binciken tasirin muhalli da zamantakewa, tare da bai wa jama'a damar bayyana ra'ayoyinsu da kuma yin cikakken nazari kan illolin tattalin arziki, lafiya da muhalli da aikin zai iya haifarwa," in ji Odayar.

  2. Mutum 9 sun mutu a rikici tsakanin jami'an tsaro da masu zanga-zanga a Kashmir

    Rahotanni daga yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi sun ce aƙalla mutum tara ne suka mutu a rikice-rikice daban-daban da suka ɓarke tsakanin jami'an tsaro da magoya bayan wata ƙungiya da gwamnati ta haramta.

    Wani jami'in yankin, Waheed Khan, ya ce jami'an tsaro sun mayar da martani ne domin kare kansu bayan da masu zanga-zangar suka kai musu hari a wurare biyu.

    Ƙungiyar ta Joint Action Committee, wadda aka haramta a watan Yuni ƙarƙashin dokokin yaƙi da ta'addanci, ta yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da wata gagarumar zanga-zanga zuwa birnin Rawalakot a ranar Laraba.

    Ƙungiyar na neman a ƙara wa yankin wakilci a siyasar ƙasar tare da yin gyare-gyare ga majalisar dokokin yankin.

    Bayanai sun nuna cewa tun bayan fara rikice-rikicen a watan Yuni, kusan mutum 30 ne suka rasa rayukansu.

  3. Zazzaɓin Lassa ya kashe mutane 221 a Najeriya

    Zazzabin Lassa

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomin lafiya a Najeriya sun bayyana damuwa kan ci gaba da yaɗuwar zazzaɓin Lassa bayan da cutar ta yi sanadin mutuwar mutum 221 a watanni shida na farkon shekarar nan.

    Alƙaluman da cibiyar dakile da yaƙi da cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta fitar sun nuna cewa an tabbatar da cutar ta kama mutum 922 a watan Yuni.

    Bayanan sun kuma nuna cewa kaso 24 cikin 100 na waɗanda suka kamu da cutar sun mutu, sama da kaso 18.7 da aka samu a daidai wannan lokaci a bara.

    Jami'an lafiya sun ce sabbin waɗanda suka kamu da cutar sun ƙaru a makonni uku a jere.

    "Daga mutum 13 da aka tabbatar sun kamu a mako na 24, adadin ya karu zuwa 22 a mako na 25, sannan ya kai 31 a mako na 26," in ji sanarwar.

    NCDC ta ce cutar ta fi bazuwa a jihohi 23 daga cikin jihohi 36 na Najeriya, inda jihohin Bauchi, Ondo, Taraba, Benue da Edo ke kan gaba wajen masu ɗauke da cutar, inda suke da kusan kashi 85 na waɗanda suka kamu da ita a bana.

    Binciken ya kuma nuna cewa matasa masu shekaru tsakanin 21 zuwa 30 su ne suka fi kamuwa da cutar, yayin da ma'aikatan lafiya ke ci gaba da fuskantar haɗari bayan an samu wasu sabbin kamuwa a tsakaninsu a makonnin baya-bayan nan.

    Zazzaɓin Lassa cuta ce da ke haddasa zubar jini, kuma tana yaɗuwa ne galibi ta hanyar abinci ko kayan gida da suka gurɓace da fitsari ko kashin wasu nau'in beraye da ke ɗauke da ƙwayar cutar.

    Haka kuma cutar na iya yaɗuwa daga mutum zuwa mutum, musamman a cibiyoyin lafiya idan ba a ɗauki matakan kariya yadda ya kamata ba.

  4. An sayar da ƙwarangwal ɗin dabbar dinosaur kan sama da dala miliyan 50

    dinosaur

    Asalin hoton, Getty Images

    An sayar da ƙwarangwal ɗin wata dabbar daji ta dinosaur nau'in da ake cewa Tyrannosaurus Rex ko T-rex a taƙaice a wani gwanjo da aka yi a New York kan sama da dala miliyan 50 - a wani sabon abin tarihi.

    Dabbar mai shekara miliyan 67 wadda ake yi wa laƙabin Gus -- na ɗaya daga cikin nau'in dinasaur mafi girma da aka samu ƙasusuwanta cikakku.

    An haƙo ƙasusuwan ne shekara biyar da ta wuce a wani gandun kiwon shanu da ke jihar South Dakota a Amurka.

    Kafin gwanjon, masana kimiyyar asalin rayuwa a ban ƙasa sun nuna damuwa cewa masu ƙazaman kuɗi za su zo su yi rububin sayen ƙwarangwal ɗin.

    Dabbar dai an ce ta rayu a doron ƙasa ne miliyoyin shekaru da suka gabata, kuma ba a samunta a wannan zamani.

  5. Gwamnatin Venezuela za ta fara tattaunawa da ƴan adawar ƙasar

    Venezuela

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin riƙon ƙwarya ta Venezuela ta ce za ta fara tattaunawa da ƴan adawar ƙasar domin ƙarfafa tafiyar da dimokraɗiyya.

    Kakakin Majalisar Dokokin Venezuela, Jorge Rodriguez, ya sanar da cewa gwamnatin za ta fara tattaunawar ne da wasu mambobin adawar daga wata mai kamawa.

    Rodriguez ya ce an cimma wannan matsaya ne domin ganin an ƙarfafa dimokuraɗiyya a ƙasar, da kuma la'akari da mummunar girgizar ƙasar da ta afku a watan da ya gabata.

    Wannan mataki na zuwa ne bayan shafe sama da watanni shida da Amurka ta kama tsohon shugaban ƙasar, Nicolás Maduro, inda mataimakiyarsa, Delcy Rodriguez, ta karɓi ragamar shugabanci a matsayin shugabar riƙon ƙwarya.

    A watan Yuni kuma, fitacciyar ƴar adawa da ke gudun hijira, Dinorah Figuera, ta kai ziyara Caracas domin tattaunawa da gwamnatin riƙon ƙwaryar.

  6. Alƙalan Kotun Ƙolin Amurka sun buƙaci a ƙara musu tsaro saboda barazanar suke fuskanta

    Wasu alƙalan Kotun Ƙolin Amurka guda biyu sun buƙaci Majalisar Dokokin ƙasar ta amince da ƙarin kuɗaɗe domin ƙarfafa musu matakan tsaro, sakamakon ƙaruwar barazanar hare-haren da suke fuskanta.

    Mai shari'a Elena Kagan da Amy Coney Barrett sun shaida wa ƴan majalisar cewa barazanar da ake yi musu yana jefa su cikin haɗurran da a baya ba a taɓa tunanin za su iya faruwa ga manyan alƙalan ƙasar ba.

    Mai shari'a Amy Coney Barrett ta ce har sai da ta kai ga yi wa ɗanta mai shekara 12 bayani abin da rigar kariya daga harsashi take nufi da kuma dalilin da ya sa dole take sanya ta.

    Rahotanni sun ce an samu ƙaruwar barazanar hare-hare ga alƙalan Amurka a wannan shekara fiye da shekarun baya.

    Saboda haka ne, bangaren shari'ar ƙasar ke neman kusan dala biliyan ɗaya domin inganta tsaron alƙalai, kotuna da kuma gidajensu.

  7. An kama mutumin da ake zargi da kafa hukumar bogi a Najeriya

    Instagram / @princeadeyemi_adeniyi

    Asalin hoton, Instagram / @princeadeyemi_adeniyi

    Jami'an tsaro sun kama mutumin da ake zargi da ƙirƙira wata hukumar ta bogi a Najeriya kuma ya naɗa kansa a matsayin Darakta Janar.

    An kama Adeniyi Adeyemi wanda ke ikirarin cewa shi ne shugaban hukumar ba da shawara kan haɓaka kasuwanci da ƙasashen ƙetare (PFIPC) bayan da mai shari'a Mohammed Umar na babbar kotun tarayya ya ba da umarnin kama shi.

    Hukumomin ƙasar sun cafke Adeyemi ne a maboyarsa da ke jihar Osun, kuma ana sa ran za a kai shi hedkwatar rundunar 'yan sanda da ke Abuja domin ci gaba da bincike da kuma shirya gurfanar da shi a gaban kotu.

    Kama Adeyemi na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan da Mai Shari'a Mohammed Umar na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya bayar da umarnin kama shi a zaman kotun na ranar Talata.

    Adeyemi bai bayyana a gaban kotun ba, duk da cewa gwamnati ta ce an riga an miƙa masa sammaci.

    Lauyan gwamnatin tarayya, Wisdom Madaki, ya shaida wa kotun cewa wannan ba shi ne karo na farko da wanda ake zargin ya ƙi halartar kotu ba, domin an riga an ɗage shari'ar har sau biyar saboda rashin zuwansa domin a gurfanar da shi.

    Saboda haka ne ya roƙi kotun ta bayar da sammacin da zai bai wa jami'an tsaro damar kamo Adeyemi tare da gabatar da shi a gaban kotu a ranar da za a ci gaba da sauraron shari'ar.

    Sai dai lauyan Adeyemi, Genesis Francis, ya ce wanda yake karewa na fuskantar barazana a rayuwarsa, kuma saboda haka ne ya kasa halartar kotun.

    Lauyan ya ƙara da cewa Adeyemi ya rubuta wata buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga Shugaba Bola Tinubu, inda ya nemi a ba shi kariya, domin a cewarsa batun ya zama abin tattaunawa a faɗin ƙasar, lamarin da ya sa ake yi masa barazana.

    Sai dai mai shari'a Mohammed Umar ya tabbatar wa lauyan cewa kotu za ta tabbatar an kare lafiyar wanda ake zargin domin ya fuskanci shari'arsa.

    Daga nan ne kotun ta amince da buƙatar masu gabatar da ƙara, kuma ta bayar da umarnin kamo Adeyemi, sannan ta ɗage sauraron shari'ar zuwa ranar 30 ga Satumba, lokacin da ake sa ran za a gurfanar da shi a gabatnta.

  8. Ana zaman ɗardar a Benue bayan kashe mutum 18

    HyacinthAlia

    Asalin hoton, HyacinthAlia/X

    Ana ci gaba da zaman dar-dar da fargaba a jihar Benue da ke tsakiyar Najeriya, bayan wani hari da aka kai a karshen mako wanda ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 18 a ƙaramar hukumar Otukpo.

    Harin ya janyo zanga-zanga daga mazauna yankin tare da ƙara jawo hankali kan hukumomi kan matsalar tsaro da ta ƙara tsananta a yankin.

    Rahotannin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato wasu mazauna yankin da jami'an gwamnati, sun ce ƴan bindigar sun kai harin ne kan masu zaman makokin jana'iza a yankin a daren Lahadi, inda suka kashe akalla mutum 18.

    Sai dai rundunar 'yan sandan jihar ta ce mutum takwas aka kashe.

    Wasu mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa maharan sun ƙona wasu gidaje, lamarin da ya fusata al'umma tare da haddasa zanga-zanga, inda suka tare hanyoyi suna neman gwamnati ta ƙara ɗaukar matakan kare rayukansu.

    Bayanai sun ce ana sa ran gwamnan jihar Benue, Rabaran Uba Hyacinth Alia, zai kai ziyara yankin da abin ya faru ranar Talata.

    Yawan hare-haren ƴan bindiga ya tilasta wa dubban mutane barin muhallansu, da kawo cikas ga harkokin noma a yankin arewa ta tsakiya da Najeriya baki ɗaya.

  9. Trump ya janye ƙudurinsa na karɓar kuɗin fito a Mashigar Hormuz

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya janye ƙudurinsa na neman jiragen ruwa da ke bi ta Mashigar Hormuz su rika biyan kuɗi ga Amurka domin tsaron da take bayarwa.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Trump ya ce bayan tattaunawa da shugabannin wasu ƙasashen Gabas ta Tsakiya, Amurka yanzu za ta fi mayar da hankali wajen samun yarjejeniyoyin kasuwanci da zuba jari maimakon karɓar kashi 20 na dukkan kayan da ake jigilarsu kamar yadda ya buƙata a baya.

    Ya kuma sake jaddada cewa mashigar ruwan a buɗe take ga dukkan jiragen ruwa.

    Sai dai bayanan zirga-zirgar jiragen ruwa na baya-bayan nan sun nuna cewa yawan jiragen da ke amfani da mashigar ya ragu a cikin watanni biyu, sakamakon ƙaruwar hare-hare tsakanin Amurka da Iran.

    Rikicin ya kuma haifar da tashin farashin mai a kasuwannin duniya.

  10. Za mu kai munanan hare-hare kan Iran idan ta takale mu - Netanyahu

    Israel's Prime Minister

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Benjamin Netanyahu

    Firaiministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya ce Isra'ila za ta kai munanan hare-haren ramuwar gayya kan Iran idan har ta sake ta kai masu hari.

    A cikin wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, Netanyahu ya ce “Ina so in faɗa wa shugabannin Iran cewa kada su yi tunanin za a ci gaba da zaman lafiya idan suka kai mana hari.”

    Ya ce martanin da Isra’ila za ta mayar ba zai zama irin na lokacin da Iran ta kai mata hari a baya ba, duk da cewa ya bayyana cewa martanin wancan lokacin “ya riga ya kasance mai ƙarfi sosai.”

    “Lokacin da ake kai mana hari ba tare da mun mayar da martani ninki biyu ba ya wuce,” in ji shi.

    Netanyahu ya ƙara da cewa ''muna yin wanan ne don magance shaiɗancin Iran, kuma za mu ci gaba da yin hakan ga duk wanda ya cutar da mu. Wannan shi ne abin da muke yi''.

  11. Hare-haren Isra'ila sun kashe mutum bakwai a Gaza

    Hukumomin lafiya a Gaza sun ce aƙalla mutum bakwai ne suka mutu bayan hare-haren da Isra'ila ta kai kan ofishin ƴansanda a Jabalia suka kashe.

    Shaidu sun shaida wa BBC cewa wani jirgi marar matuƙi na Isra'ila ya harba makamai masu linzami huɗu a wani ofishin ƴansanda da ke kusa da wata kasuwa mai cunkoso.

    Ma'aikatar harkokin cikin gida da ke aiki ƙarƙashin Hamas a Gaza ta ce ɗaya daga cikin waɗanda aka kashen shugaban ofishin ƴansandar ne.

    Daga cikin waɗanda suka mutu har da wata mace. Kawo yanzu dai sojojin Isra'ila ba su ce komai kan hakan ba.

  12. Jami'an kashe gobara na fafatawa da gobarar daji a Faransa

    Gobarar daji

    Asalin hoton, Frank Desprez / SDIS 77 via EPA

    Gobarar daji da ke ci gaba da bazuwa a wani daji da ke kudancin birnin Paris ta mamaye kusan murabba’in kilomita ashirin, yayin da jami’an kashe gobara ke fatan shawo kanta a yau.

    Ministan harkokin cikin gidan Faransa ya ce an kama mutum biyu bisa zargin haddasa gobarar da gangan.

    Ɗaya daga cikinsu matashi ne mai shekara 18, wanda rahotanni suka ce an kama shi ɗauke da abin kunna wuta, yayin da hannayensa ke cike da toka.

    A faɗin ƙasar, an kama mutane 59 bisa zargin haddasa gobara da gangan ko kuma sakaci.

    A karon farko a yankin Paris, an tura jiragen sama na musamman da jirage masu saukar ungulu masu zubar da ruwa domin taimakawa wajen dakile gobarar.

  13. Wa zai kai wasan ƙarshe tsakanin Faransa da Spain?

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Kylian Mbappe da Lamine Yamal za su fuskanci junansu karo na 11, sai dai wannan ne karawa mafi muhimmanci saboda suna neman zuwa wasan ƙarshe na Gasar Kofin Duniya.Ga wasu bayanai kan hamayyar da ke tsakanin ƴan wasan da kuma ƙasashensu.

  14. An gargaɗi jiragen Turai game da keta sararin samaniyar ƙasashen Gulf

    Hoton jirgi

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da kariyar jiragen sama ta Tarayyar Turai ta gargaɗi jiragen sama kan keta sararin samaniyar ƙasashen Bahrain da Kuwait da Qatar UAE da kuma ratsawa ta saman tekun Oman.

    Hukumar ta ce ta yi gargaɗin ne saboda halin rashin tabbas da ake ciki a yankin kan ƙaruwar ayyukan soji ciki har da yiwuwar samun makamn linzami da jirage marasa matuƙa.

    ''Akwai yiwuwar fuskantar hatsari wajen ketawa ta saman wannan yanki'', in ji hukumar.

    Hukumar ta ce za a ci gaba da aiki da wannan shawara har zuwa ranar 29 ga watan Yulin, inda ta ce za ta ci gaba da sanya idanu kan lamarin.

    Ƙasashen yankin na fama da hare-haren Iran kan sansanonin sojin Amurka a yankin, yayin da Amurka ke amfani da ƙasashen wajen kai wa Iran hare-hare.

  15. Farashin ɗanyen man fetur ya zarce dala 85

    gangar mai

    Asalin hoton, Getty Images

    Yayin da yaƙi tsakanin Amurka da Iran ke ci gaba da zafafa, farashin man feutur a kasuwannin duniya na ci gaba da yin tashin gwauron zaɓo.

    A ranar Talata farashin ya tashi da kusan kashi uku cikin ɗari, lamarin da ya sa man ya yi tsada mafi yawa cikin mako huɗu.

    Tashin farashin ba ya rasa nasaba da barazanar Amurka na datse tasoshin ruwan Iran.

    Barazanar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen biyu ke zafafa hare-haren ramuwar gayya kan kan ƙoƙarin ƙwace iko da mashigar Hormuz.

  16. ADC da Atiku sun ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Koli

    Atiku

    Asalin hoton, Atiku/X

    Jam'iyyar ADC a Najeriya da kuma ɗantakararta na shugaban ƙasa, Atiku Abubakar sun yanke shawarar ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙolin Najeriya kan hukuncin shugabancin jam'iyyar.

    A ranar Litinin ne kotun ɗaukaka ƙara da umarci hukumar zaɓen ƙasar INEC ta daina amincewa da tsagin David Mark a matsayin shugabannin jam'iyyar.

    Cikin wasu mabambantan sanarwa da ADC da Atiku suka fitar, sun ce za su ƙalubalanci hukuncin a Kotun Ƙolin ƙasar.

    Kotun ɗauka ƙarar ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya wadda ta hana INEC amincewa da tarukan jam'iyyar na ƙasa da jihohi, wanda a nan ne aka zaɓi shugabannin ɓangaren David Mark.

    Atiku da ADC sun buƙaci lauyoyinsu su tattara duka bayanan da suke buƙata domin ɗaukaka ƙarar.

    ADC ta jima tana fama da rikicin shugabanci, wani abu da masana ke gani a matsayin barazana ga shirye-shiryen jam'iyyar don tunkarar zaɓen 2027.

    Atiku Abubakar

    Asalin hoton, Atiku Abubakar

  17. An kai hare-hare a wurare huɗu a birnin Bushehr na Iran

    Mataimakin gwamnan lardin Bushehr mai kula da harkokin tsaro ya ce an kai hare-hare a wurare huɗu da ke cikin birnin Bushehr.

    Ehsan Jahanian ya ce hare-haren sun faru ne da yammacin ranar Litinin agogon ƙasar Iran.

    Ya ce binciken farko da aka gudanar, sun nuna cewa babu rahoton asarar rayuka sakamakon hare-haren.

    Tun da farko kuma, gidan talabijin na ƙasar Iran ya ruwaito cewa an ji ƙarar fashewa har sau biyar a yammacin birnin Bandar Abbas.

    Hare-haren sun faru ne sa'o'i kaɗan bayan Rundunar Sojin Amurka ta CENTCOM ta sanar da kammala wani sabon jerin hare-haren da ta kai kan Iran.

  18. Dangote ya dakatar da sayar da man fetur da naira

    Dangote

    Asalin hoton, Dangote Refinery

    Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da mai ga masu sari da kuɗin Najeriya naira.

    A ranar 1 ga watan Oktoban 2024 ne dai Dangote ya fara sayar da mai na naira ga kwastomominsa a Najeriya, bayan cimma wata yarjejeniya da gwamnatin ƙasar, kan wadata ƙasar da man fetur.

    A lokacin an cimma yarjejeniyar cewa gwamnatin Najeriya za ta riƙa sayar masa da ɗanyen mai da naira yayin da shi ma zai riƙa sayar da wanda ya tace da naira.

    Kawo yanzu dai babu wata ƙwaƙƙwarar hujja da Dangoten ya bayar dangane da wannan mataki, to amma wasu jaridun ƙasar na ambato wasu majiyoyi a matatar na cewa a yanzu gwamnati na sayar da matatar ɗanyen mai ne da dala, kuma ba ta sayar mata wanda zai wadace ta.

  19. An ji ƙarar manyan abubuwan fashewa a Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayar da rahoton jin ƙarar abubuwan fashewa a birnin Bandar Abbas mai gaɓar ruwa, yayin da yaƙi tsakaninta da Iran da Amurka ya tsananta kan iko da mashigar Hormuz.

    Amurka ta ce ta ƙaddamar da hare-hare kan cibiyoyin soji a faɗin Iran cikin dare, domin ruguza ƙarfinta wajen kai wa jiragen ruwa hare-hare.

    A nata ɓangare Iran ta ce ta kai hare-hare kan cibiyoyin sojin Amurka a Bahrain da Jordan, bayan wasu hare-hare da ta kai wa wasu manyan jiragen ruwa a mashigar Hormuz

  20. Sojojin Jordan sun ce sun kakkaɓo makaman Iran

    Rundunar sojin Jordan ta bayyana cewa ta kakkaɓo wasu makaman linzami huɗu da Iran ta harba mana.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar, ta ce dakarun juyin juya halin Iran sun tabbatar da kai hari kan sansanin sojin Amurka da ke Jordan.

    A ƴan kwanakin nan Iran ta riƙa kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da ƙasashen yankin Gulf, a matsayin martani kan hare-haren da Amurka ta kai mata.

    Ko a safiyar yau Talata sai da rundunar IRGC ta bayyna cewa ta kai hari kan cibiyar sadarwar tauraron ɗan'adam ta Amurka da sansanin sojin Amurka da ke Bahrain.