Tattaunawar Lebanon da Isra'ila ta ƙare ba tare da cimma matsaya kan janye sojoji ba
Jami'an Lebanon da Isra'ila sun kammala wata tattaunawa ta bayan fage da Amurka ta shirya a birnin Rome na Italiya, ba tare da cimma matsaya kan takamaiman lokacin da sojojin Isra'ila za su fice daga kudancin Lebanon ba.
A wata yarjejeniya da ɓangarorin suka fitar a watan da ya gabata, sun amince da fara janyewar Isra'ila daga wasu yankuna na farko a kudancin Lebanon.
Yarjejeniyar ta kuma tanadi kwance ɗamarar ƙungiyar Hezbollah, da kuma maye gurbin sojojin Isra'ila da dakarun gwamnatin Lebanon a yankunan da abin ya shafa.
Sai dai wakilin BBC ya ce jami'an Lebanon sun nuna rashin gamsuwa da sakamakon tattaunawar, saboda suna ganin ba za a samu wani ci gaba ba kafin gudanar da zaɓen Isra'ila da ake sa ran yi a watan Oktoba.




























